التصنيفات
القرآن الكريم

المختصر في التفسير Hausa سورة [التحريم]

وَمَرۡيَمَ ٱبۡنَتَ عِمۡرَٰنَ ٱلَّتِيٓ أَحۡصَنَتۡ فَرۡجَهَا فَنَفَخۡنَا فِيهِ مِن رُّوحِنَا وَصَدَّقَتۡ بِكَلِمَٰتِ رَبِّهَا وَكُتُبِهِۦوَكَانَتۡ مِنَ ٱلۡقَٰنِتِينَ

الهوساوية | Hausa

Allah ya bugawa (sanya wa) waxanda suka yi imani da Allah da manzanninsa misali da halin Nana Maryam yar Imrana, wadda ta kiyaye farjinta daga aikata zina, sai Allah ya umarci malaika Jibrilu ya yi busa a jikinta, sai ta xauki cikin Annabi Isa da ikon Allah ba tare da uba ba, kuma ta gaskata da sharioin Allah, da littattafansa, waxanda ya saukar wa manzanninsa, kuma ta kasance daga cikin masu yi wa Allah xaa, ta hanyar kamanta umarninsa, da nisantar abubuwan da ya hana.